IQNA

An Rufe Wuraren Ziyara Na Addini A Kasar Masar

23:59 - March 16, 2020
Lambar Labari: 3484630
Tehran (IQNA) mahukunta a kasar Masar sun sanar da rufe dukkanin wurare na ziyara ta adini a kasar domin kaucewa yaduwar cutar corona a tasakanin jama'a.

Tashar CNN ta bayar da rahoton cewa, a cikin wani bayani da gwamnatin Masar ta fitar a yau an bayyana cewa, daga yau an rufe dukkanin wurare na ziyara ta addini a kasar domin kaucewa yaduwar cutar corona a tasakanin jama'ar kasar.

Dauka wannan mataki dai ya zo ne bayan tattaunawa tare da malaman adini, da uam samun umarni daga babban malamin cibiyar ahzar Sheikh Ahmad Tayyib, da kuma malaman darikun sufaye.

Sanarwar ta ce wannan mataki na takaitaccen lokaci ne, wanda zai kawo karshe da zaran an samu saukin yaduwar cutar corona wadda ta addabi duniya a halin yanzu.

A daya bangaren cibiyar Azhar ta sanar da dakatar da dukkanin sallolin jam'i a masallatan kasar, kamar yadda aka dakatar da taruka na addini baki daya.

3885864

 

 

 

Abubuwan Da Ya Shafa: masar ziyarar arbaeen wyur kasar masar
captcha